Ambaliyar ruwa ta lalata gidaje sama da 100 a Jos

Mazauna kusan gidaje sama da 100 ne ambaliyar ruwa ta raba da gidajensu a unguwannin Rikkos, Bauchi Road, Anguwan Rogo da kuma Naraguta dake karamar hukumar Jos North.

An samu ambaliyar ruwan ne biyo bayan mamakon ruwan sama da aka samu a ranar Asabar da kuma Lahadi.

Wani mazaunin Bauchi Road mai suna Tanko Aliyu ya fadawa manema labarai cewa ba a samu asarar rayuka a ambaliyar ba amma kuma ta raba mutane da dama da gidajensu inda a yanzu suke zaune tare da yan uwansu.

Salamatu Aliyu É—aya daga cikin waÉ—anda abun ya shafa ta bayyana cewa basu taba tsammanin ambaliyar ruwan za ta faru ba har ta kai ta raba ta gidanta ita da makociyarta dake Anguwar Rogo inda tayi kira ga gwamnati kan ta kawo musu dauki.

More News

Kotu ta É—aure mutumin sa ya yi sama-da-faÉ—i da kuÉ—in marayu

Babbar kotu a jihar Borno ta yanke wa Isiyaku Ibrahim hukuncin shekara ɗaya a gidan yari da zaɓin biyan tarar naira dubu 100 saboda...

NFF ta naÉ—a Finidi George a matsayin sabon kocin Super Eagle

An naɗa Finidi George a matsayin sabon mai horar da kungiyar ƙwallon ƙafar Najeriya wato Super Eagle. Hukumar ƙwallon Ƙafa ta Najeriya, NFF ita ta...

Gwamnan Edo Zai Fara Biyan 70,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

Gwamnan jihar Edo, Godwin Obaseki ya sanar da mafi ƙarancin albashi ga ma'aikatan ga ma'aikatan jihar inda za a riƙa biyan naira dubu 70,000. Gwamnan...

JAMB ta fitar da sakamakon jarabawar 2024

Hukumar shirya jarabawar shiga makarantun gaba da sakandire ta JAMB, ta fitar da sakamakon jarrabawar shekarar 2024, watau sakamakon UTME.Sama da mutane miliyan 1.94...