Matakin da rundunar ‘yan sandan Najeriya ta dauka na rusa sashenta da ke yaki da fashin da makami, wanda aka fi sani da SARS a takaice, ya sanya ‘yan kasar murna matuka.
Gabanin wannan mataki, ‘yan Najeriya sun kwashe shekara da shekaru suna fafutukar ganin an rusa rundunar SARS, wadda ake zargi da cin zarafi da azabtarwa da ma kashe mutanen da ta kama.
Sai dai wani muhimmin abu da ya fito fili tun bayan rusa SARS shi ne irin rawar da masu fafutuka suke takawa wurin kawo sauyi a duniya.
Aisha Yesufu na cikin mutanen da suka kwashe shekara da shekaru suna fafutukar ganin an samar da mulki na gari a Najeriya, kuma sunanta ya kara fitowa fili a lokacin da ta shige gaba wajen fafutukar ganin an ceto ‘yan matan makarantar Chibok da mayakan Boko Haram suka sace a 2014.
A wannan karon ma, ta taka muhimmiyar rawa a zanga-zangar kyamar SARS inda wani hotonta da ta bijirewa ‘yan sanda ya karade shafukan intanet na kasar.
Wani abu da ya bambanta ta wajen wannan fafutuka shi ne yadda ake saukin gane ta saboda ko da yaushe tana sanye da hijabi.
Wace ce wannan mata da ke son kawo sauyi a Najeriya?
An haifi Aisha Yesufu a 1973 a birnin Kano da ke arewacin Najeriya kuma a birnin ta girma.
‘Yar asalin jihar Edo da ke kudu maso kudancin kasar ce.
Ta yi karatunta na Digiri a Jami’ar Bayero da ke Kano a fannin Microbiology.
‘Yar fafutukar tana da aure da ‘ya’ya.
“Ina bala’in son mijina,” a cewar Aisha wadda ta kara da cewa mijinta ba ya zuwa wurin da take fafutuka saboda shi ba mai son hayaniya ba ne.