Adadin waɗanda suka mutu sakamakon ambaliyar ruwa a Libya ya zarce 6,000

Hukumomin Libya sun ce adadin mutanen da suka mutu sakamakon ambaliyar ruwa da guguwa a kasar ya zarce 6,000.

Sabbin alkaluman da gwamnatin Libiya ta fitar a ranar Larabar sun kara da cewa har yanzu dubban mutane ne suka bace sakamakon wannan mummunan lamari.

A cewar hukumar Majalisar Dinkin Duniya sama da mutane 30,000 ne suka rasa matsuguni sakamakon ambaliyar ruwa.

Wannan na zuwa ne bayan wata mummunar girgizar kasa ta afku a ƙasar Morocco inda sama da mutum 2,000 suka rasa rayukansu, tare da hasarar dukiya.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]