Adadin waɗanda suka mutu sakamakon ambaliyar ruwa a Libya ya zarce 6,000

Hukumomin Libya sun ce adadin mutanen da suka mutu sakamakon ambaliyar ruwa da guguwa a kasar ya zarce 6,000.

Sabbin alkaluman da gwamnatin Libiya ta fitar a ranar Larabar sun kara da cewa har yanzu dubban mutane ne suka bace sakamakon wannan mummunan lamari.

A cewar hukumar Majalisar Dinkin Duniya sama da mutane 30,000 ne suka rasa matsuguni sakamakon ambaliyar ruwa.

Wannan na zuwa ne bayan wata mummunar girgizar kasa ta afku a ƙasar Morocco inda sama da mutum 2,000 suka rasa rayukansu, tare da hasarar dukiya.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]