Adadin Masu Coronavirus a Najeriya Ya Doshi 5000 | VOA Hausa

Sabbin alkaluman da hukumar dakile yaduwar cututtuka a Najeriya ta NCDC ta fitar, sun yi nuni da cewa mutum 146 sun sake kamuwa da cutar cikin yinin jiya Talata.

Har yanzu dai Legas ce ke kan gaba wajen samun yawan masu dauke da cutar, inda yanzu ta sake samun sabin mutum 57.

Baya ga Legas, jihar Kano wacce ta ke fama da yawan mace-mace a ‘yan kwanakin nan ita ma ta samu mutum 27 da suka kamu da cutar.

Ya zuwa yanzu adadin masu cutar ya kai 4,787 a duk fadin kasar.

Adadin masu rasuwa sakamakon cutar shi ma yana dada haurawa, inda a cikin yinin jiya kawai aka samu mutum 8 da suka mutu sakamakon cutar.

Hakan ya mayar da adadin wadanda coronavirus ta kashe zuwa 158.

Masu samun waraka su ma sun kara yawa, inda yanzu Najeriya ke da mutum 959 da suka warke daga cutar.

More News

Ƴan bindiga sun Æ™one ginin hedkwatar Æ™aramar hukuma tare da kashe jami’an tsaro

Ƴan bindiga sun kai farmaki hedkwatar ƙaramar hukumar, Isiala Mbano dake jihar Imo da tsakar daren ranar 3 ga watan Satumba inda suka ƙone...

An kama wasu Æ´anta’adda da ke da alaÆ™a da Turji

Akalla mayaka 18 da ke da alaka da fitaccen shugaban ‘yan ta’adda Bello Turji aka kama a jihar Sokoto da ke arewa maso yammacin...

Dakarun Najeriya sun kai farmaki wa Æ´an’adda a Borno, wani kwamanda ya miÆ™a wuya

Rundunar sojin Najeriya ta sanar a ranar Lahadin cewa dakarunta sun yi nasarar kashe wani fitaccen kwamandan kungiyar Boko Haram, Abu Rijab da wasu...

Yadda wani adalin direba ya kawo cigiyar haka maƙare a kuɗi

Wani direban motar kasuwa ya mayarwa rundunar ‘yan sandan jihar Kano jakar da ta bata dauke da makudan kudade.  Direban mai suna Safiyanu Mohammed...