Sarkin manoman jahar Nasarawa, Alhaji Aliyu Usman yace dalibai da suka kamala karatu basu da ayyukan yi, zasu sami guraben aiki a kamfanin.
Basaraken gargajiya na yankin Awe, Alhaji Abubakar Umar na biyu yace jama’a da dama sun yi na’am da shirin don fiye da matasa dubu daya yanzu suna aiki a gonar, wanda an dauke su aiki kenan.
Ana sa nan da shekaru biyu zuwa uku kamfanin zai fara aiki tukuru.









