Qatar Ta Musanta Shirya Ganawar Iran Da Amurka A Doha



Gwamnatin Qatar ta bayyana cewa babu wani babban jami’in Iran da ke birnin Doha a halin yanzu domin tattaunawar zaman lafiya, duk da isar manyan wakilan shugaban Amurka Donald Trump zuwa kasar.

Mai magana da yawun Ma’aikatar Harkokin Wajen Qatar, Majid Ansari, ya ce Steve Whittaker da Jared Kushner sun isa Doha ne domin ganawa da masu shiga tsakani tare da tattauna wasu batutuwan yankin, ciki har da halin da ake ciki a Lebanon.

Ansari ya jaddada cewa babu wata ganawa da aka shirya tsakanin Iran da Amurka a kwanaki masu zuwa.

Bayanin na Qatar ya yi daidai da matsayar jami’an Iran, amma ya saba da kalaman Donald Trump wanda ya ce za a gudanar da wata muhimmiyar ganawa tsakanin Amurka da Iran a Doha bisa bukatar Tehran.

Tun da farko Iran ta bayyana cewa babu wata tattaunawa da aka tsara tsakaninta da Amurka, tana mai cewa ziyarar da jami’anta za su kai Doha na da nasaba ne da batun kudaden kasar da aka kwace.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]