Trump Ya Ce Iran Ta Nemi Ganawa Da Amurka A Qatar



Shugaban Amurka Donald Trump ya bayyana cewa Iran ta nemi gudanar da wata ganawa da Amurka a birnin Doha na ƙasar Qatar, bayan tashin hankalin da ya biyo bayan hare-haren da ƙasashen biyu suka kai wa juna.

Fadar White House ta ce jami’an Amurka Jared Kushner da Steve Witkoff za su halarci taron, yayin da Trump ke fatan ci gaba da tattaunawar sulhu tsakanin ɓangarorin.

Sai dai mataimakin ministan harkokin wajen Iran, Kazem Gharibabadi, ya musanta batun gudanar da ganawar a wannan makon. Ya ce har yanzu ba a kammala shirye-shiryen ranar ko wurin taron ba, duk da cewa masu shiga tsakani na ci gaba da tattaunawa.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]