Hare-Haren ‘Yan Bindiga Sun Yi Sanadin Mutuwar Mutane Hudu Da Sace Matafiya A Zamfara


Akalla mutane hudu sun mutu yayin da wasu matafiya suka fada hannun masu garkuwa da mutane a wasu hare-hare da ake zargin ‘yan bindiga ne suka kai a Karamar Hukumar Zurmi da ke Jihar Zamfara.

Rahotanni sun nuna cewa mutane uku, wadanda suka hada da mazauna garin Zurmi biyu da wani mutum daga wani kauye makwabta, sun rasa rayukansu yayin da suke aiki a gonakinsu.

Haka kuma, an ruwaito cewa wasu ‘yan bindiga sun kai hari kauyen Baichen Dauran inda suka kashe mutum guda.

A wannan dare ne kuma aka ce an yi garkuwa da wasu matafiya a wata hanya da ke kusa da kauyen, ciki har da wani direban mota na kasuwanci daga Zurmi mai suna Kabiru Takaye.

Mazauna yankin da kewaye na ci gaba da nuna damuwa saboda yawaitar hare-haren da ke barazana ga rayuka da hanyoyin samun abinci da kudin shiga.

Har zuwa lokacin hada wannan rahoto, gwamnatin Jihar Zamfara da hukumomin tsaro ba su fitar da wata sanarwa a hukumance kan lamarin ba.

More from this stream

Recomended