
Asalin hoton, Getty Images
Rahotanni daga arewacin babban birnin Iran na Tehran na cewa an ji wata kara mai karfin gaske, ta fashewar wasu abubuwa da ba a kai ga gano su ba kawo yanzu.
Lamarin ya faru ne a cikin dare a Mellat, wani sanannen wuri da ke kusa da hedkwatar kamfanin watsa labarai birin.
Mataimakin gwamnan Teheran ya ce zuwa yanzu mahukunta na ci gaba da bincike don gano ainihin abun da ya faru.
Kawo yanzu dai babu rahoton mutuwar wani ko jikkatar mutane, sai dai hotunan bidiyo a shafukan sada zumunta sun nuna yadda hayaki ya turnuke wajen.
Daga shekarar 2020 ne aka fara samun karuwar hare-haren ban mamaki da suka tarwatsa muhimman wurare a Iran, yawanci wadanda Iran ke amfani da su wajen inganta shirinta na Nukiliya..
An samu tashin gobara da dama da suka lalata kayayyaki a cibiyar nukiliya, matatun mai da cibiyar samar da wutan lantarki, kamfanoni da wuraren kasuwanci a fadin kasar.
Ga wasu daga cikinsu da aka samu a 2020.
(BBC Hausa)