

Daramola yace an kaddamar da bincike don fayyace abin da ya faru, da irin rawar da sojojin suka taka, kuma muddin an same su da laifi, to tabbas za a dauki kwararan matakai akan su.
A cewar wani masanin harkar sojin sama, Wing Commander M. Salman, domin irin wannan yanayi aka kafa kotun soji, wacce zata gudanar da shari’a idan har an sami jami’an da laifi.
Wannan matsalar dai tuni ta fara jan hankalin lauyoyin kare hakkin bil adama, irin su Lauya Yakubu Saleh Bawa, wanda yace zasu sa ido don ganin yadda binciken zai kasance.