![](https://arewa.ng/storage/img-20240613-wa00047677152431271958559-600x399.jpg)
Jami’an ‘yan sanda daga babban birnin tarayya Abuja sun kashe wani dan bindiga tare da cafke uku a wani samame da suka kai.
Ƴan sandan sun kai samamen ne a wata maboyar masu garkuwa da mutane a garin Chikara da ke kan iyaka da jihar Kogi.
Duk da haka, wannan ya haifar ba-ta-kashi tsakaninsu da ƴansandan.
A wata sanarwa da rundunar ‘yan sandan ta fitar a ranar Asabar ta hannun mai magana da yawunta a Abuja, Josephine Adeh, ta bayyana wadanda ake zargin a matsayin Mahammadu Isa, Likita Idris, da Isiyaku Muhammedu.