Ƴan sandan jihar Bauchi sun kama mutum 9 da ake zargi da fashi da makami

‘Yan sanda a jihar Bauchi sun yi nasarar cafke wasu mutane tara da ake zargi da aikata laifin fashi da makami da addabar mazauna jihar.

Kakakin rundunar ‘yan sandan SP Ahmed Wakil ne ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ya raba wa manema labarai ranar Laraba a Bauchi.

Ya kara da cewa, an samu nasarar cafke wadanda ake zargin ne ta hanyar bajintar kokarin hadin gwiwa na Operation Restore Peace, ORP, da Rapid Response Squad, RRS, na rundunar.

Wakili ya ce, “Game fa aikin sahihan bayanan sirri game da ayyukan kungiyar ‘yan fashi da makami a yankin jami’an suka dauki matakin gaggawa.

“Kungiyoyin sun kasance a karkashin jerin sunayen da ƴan sanda suke son kamawa saboda hannu a fashi da makami.

“A ranar 13 ga Agusta, 2023, da misalin karfe 15:03, ORP ta kama wasu mutane uku da ake zargin ‘yan fashi da makami ne da suka addabi yankin Bauchi.”

Ya kara da cewa kwamishinan ‘yan sandan jihar Bauchi ya umurci mutanensa da su ci gaba da gudanar da bincike kan irin wadannan miyagun ayyuka a jihar.

More News

Kotu ta ɗaure mutumin sa ya yi sama-da-faɗi da kuɗin marayu

Babbar kotu a jihar Borno ta yanke wa Isiyaku Ibrahim hukuncin shekara ɗaya a gidan yari da zaɓin biyan tarar naira dubu 100 saboda...

NFF ta naɗa Finidi George a matsayin sabon kocin Super Eagle

An naɗa Finidi George a matsayin sabon mai horar da kungiyar ƙwallon ƙafar Najeriya wato Super Eagle. Hukumar ƙwallon Ƙafa ta Najeriya, NFF ita ta...

Gwamnan Edo Zai Fara Biyan 70,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

Gwamnan jihar Edo, Godwin Obaseki ya sanar da mafi ƙarancin albashi ga ma'aikatan ga ma'aikatan jihar inda za a riƙa biyan naira dubu 70,000. Gwamnan...

JAMB ta fitar da sakamakon jarabawar 2024

Hukumar shirya jarabawar shiga makarantun gaba da sakandire ta JAMB, ta fitar da sakamakon jarrabawar shekarar 2024, watau sakamakon UTME.Sama da mutane miliyan 1.94...