Ƴan sanda sun kama wani mutum ɗauke da bindigogi 20 a Kaduna

Rundunar ƴan sandan jihar Kaduna ta ce jami’anta sun kama wani  riƙaƙƙen mai safarar bindiga inda aka same shi da bindigogin AK-47 ƙirar gida guda 20.

A wata sanarwa ranar Juma’a mai magana da yawun rundunar ƴan sandan jihar Kaduna ya ce wanda aka kama ɗin mai suna, Bitrus Gyang ya fito ne daga Barikin Ladi a jihar Filato kuma an kama shi a Buruku dake ƙaramar hukumar Igabi  ta jihar Kaduna.

Ya ce an kama Gyang ne a ranar Alhamis lokacin da jami’an tsaro suke gudanar da binciken ababen hawa da suka saba a gadar Buruku.

Mai magana da yawun rundunar ya bayyana cewa  a lokacin da Gyang yake amsa tambayoyi ya faɗi cewa yana safarar bindigogi kuma wannan ne karo na uku.

Hassan ya ƙara da cewa kwamshinan ƴan sandan jihar, Ali Dabagi ya yabawa jami’an ƴan sandan kan sadaukarwar da suka nuna.

More News

An kama wasu mutane biyu da hodar ibilis a Lagos

Rundunar ƴan sandan jihar Lagos ta sanar da kama wasu mutane biyu da aka samu ɗauke da ƙunshin hodar ibilis mai yawan gaske. Mai magana...

Kwankwaso ya bada tallafin miliyan ₦50 ga mutanen da ambaliyar Borno ta shafa

Tsohon gwamnan jihar Kano kuma jagoran jam'iyar NNPP, Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso ya bada tallafin naira miliyan 50 ga mutanen da ambaliyar ruwa a...

Sakamakon NECOn 2024 ya fito

Hukumar shirya jarabawar ta kasa ta fitar da sakamakon jarabawar kammala sakandare ta watan Yuni/Yuli 2024, inda kashi 60.55 cikin 100 na waɗanda suka...

Ƴan Najeriya na shan baƙar wahala—Janar Abdulsalami

Tsohon shugaban kasa, Janar Abdulsalami Abubakar, ya ce wahalhalun da ake fama da su a Najeriya na kara tabarbarewa, kuma rabon kayan agajin ba...