Ƴan bindiga sun yi awon-gaba da ɗaliban jami’ar Dutsinma

Rahotannin da muke samu na nuna cewa ƴan bindiga sun sace kimanin dalibai mata biyar na jami’ar da ke Dutsinma a jihar Katsina.

BBC ta gano cewa lamarin ya faru ne a cikin dare da misalin karfe biyu a ɗakunan kwanan da dalibai ke kamawa a wajen makarantar.

Jami’in kula da jama’a na ƴan sanda a jihar, ASP Abubakar Sadiq Aliyu ya shaida wa BBC cewa a halin yanzu sun sami nasarar kama mutum daya da ake zargi da hannun sa a sata da garkuwa da ɗaliban.

“A halin yanzu kuma muna ƙara faɗaɗa bincike don kama sauran mutane da ke da hannu a wannan aikin.”

More News

Dakarun Najeriya sun cafke wasu ƴan’aiken ƴanbindiga a Kaduna

Sojoji sun kama wasu mutum biyu da ake zargi da kaiwa 'yan bindiga sakonninsu a kasuwar ƙauyen SCC da ke ƙaramar hukumar Kachia a...

Ƴansanda sun hallaka masu garkuwa da mutane

Ƴansanda sun hallaka wasu masu garkuwa da mutane uku da ake zargin sun yi yunkurin yin garkuwa da matar wani dan majalisar dokokin jihar...

Ƴanbanga sun sake kawar da wani ƙasurgumin ɗanbindiga

Rahotanni da ke fitowa daga Arewa maso Yammacin Najeriya na nuna cewa an yi nasarar kawar da wani fitaccen dan bindiga a jihar Zamfara,...

Ƴansanda a Katsina sun yi nasarar cafke wasu tantiran masu safarar alburusai wa ƴanbindiga

Rundunar ‘yan sandan jihar Katsina a ranar Juma’a ta sanar da cewa ta kama wasu manyan ‘yan bindiga guda uku tare da kwato manyan...