Ƴan bindiga sun kashe sarakuna biyu a jihar Ekiti

Wasu da ake zargin masu garkuwa da mutane ne sun kashe sarakuna biyu a jihar Ekiti a ranar Litinin.

Sarakunan biyu na kan hanyarsu ne ta dawowa daga wani taro da suka halarta a Irele-Ekiti inda aka biyo sawunsu aka bindige su har lahira.

Oba David Ogunsakin, mai rike da sarautar Elesun na Esun-Ekiti; da kuma Oba Olatunde Olusola, mai rike da sauratar Onimojo na Omojola-Ekiti sune sarakunan da aka kashe.

Sunday Abutu mai magana da yawun rundunar yan sandan jihar ya tabbatar kisan sarakunan biyu.

Abutu ya kara da cewa tuni aka tura tawagar jami’in sirri na rundunar ya zuwa yankin.

Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya NAN ya rawaito cewa Oba Adebayo Fatoba, Alara na Ara-Ekiti ya tsira da ransa a harin.

Da yake mayar da martani kan faruwar lamarin gwamnan jihar Ekiti Biodun Oyebanji ya umarci rundunar Æ´an sandan jihar su zakulo wadanda suka aikata laifin.

More News

Manyan dillalan mai za su fitar da litar man fetur miliyan 300 a wannan makon

Ƙungiyar MEMAN ta manyan dillalan man fetur da dangoginsa ta ce mambobinta sun fara lodin mai har lita miliyan 300 a cikin makon nan...

Kotu ta É—aure mutumin sa ya yi sama-da-faÉ—i da kuÉ—in marayu

Babbar kotu a jihar Borno ta yanke wa Isiyaku Ibrahim hukuncin shekara ɗaya a gidan yari da zaɓin biyan tarar naira dubu 100 saboda...

NFF ta naÉ—a Finidi George a matsayin sabon kocin Super Eagle

An naɗa Finidi George a matsayin sabon mai horar da kungiyar ƙwallon ƙafar Najeriya wato Super Eagle. Hukumar ƙwallon Ƙafa ta Najeriya, NFF ita ta...

Gwamnan Edo Zai Fara Biyan 70,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi

Gwamnan jihar Edo, Godwin Obaseki ya sanar da mafi ƙarancin albashi ga ma'aikatan ga ma'aikatan jihar inda za a riƙa biyan naira dubu 70,000. Gwamnan...