Kungiyar Kwadago ta Najeriya NLC ta caccaki gwamnatin tarayya a kan tallafin da ta bayar wa jihohi bayan cire tallafin man fetur.
Idan ba manta ba, Gwamnatin Tarayya a watanni baya ta cire tallafin man fetur, ta kuma baiwa gwamnatocin jihohi tallafin abinci don ci gaba da rabawa ‘yan Najeriya tare da Naira biliyan 5.
Sai dai sa’o’i bayan ayyana yajin aikin kwanaki biyu a fadin kasar sakamakon illolin cire tallafin man fetur, shugaban NLC, Joe Ajaero, ya ce rabon kayan abinci bai wadatar ba wajen yaki da illar matakin da gwamnati ta dauka.
“Idan kun raba wannan N5bn ko ma manyan motoci biyar na shinkafa ko hatsi, mutane da yawa ba za su samu kofin shinkafa daya ko rabin ba,” in ji shi.
“Idan ka raba N5bn, mutane da yawa, watakila a cikin ma’aikata ko talakawa, ba za su samu N1,500 ba. Yanzu, wannan shi ne tallafin?”