Ƴansanda sun yi nasarar kama sojan bogi

Rundunar ‘yan sandan jihar Legas ta ce ta kama wani sojan bogi da ake zargi da aikata laifukan yaki, wanda sojoji suka bayyana suna nema ruwa a jallo.

Kakakin rundunar ‘yan sandan, SP Benjamin Hundeyin, wanda ya tabbatar wa Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya, an kama wanda ake zargin ne a ranar Asabar da misalin karfe 3:00 na rana a unguwar Ijegun da ke Legas.

Mista Hundeyin ya ce an kama wanda ake zargin ne a yayin wani sintiri na yau da kullun da rundunar ‘yan sanda ta Ijegun ta yi a unguwar Fagbile Estate, Ijegun, a Sherin Oshun.

Ya ce rundunar ‘yan sintiri ta kama mutumin mai suna Sajan Manjo (wannan wani suna ne da aka sakaye), cikin kakin soja, wanda ake zargin an yi amfani da shi wajen yin katsalandan.”

“Nan da nan muka aika a kirawo kwamandan tsaron sojan da ke jagorantar bututun mai a Ijeododo, domin ya zo ya tantance wanda ake zargi.

“Sojoji sun tabbatar da cewa sojan bogi ne.  A yayin da ake yi masa tambayoyi, wanda ake zargin ya tabbatar da aikata laifin.

“Sojoji sun tabbatar da cewa yana cikin jerin sunayen da ake nema ruwa a jallo. Za a gurfanar da shi a kotu idan an kammala bincike,” inji shi.

More News

Zanga-zanga: An jibge ƴan sanda 4200 a Abuja

Rundunar ƴan sandan birnin tarayya Abuja ta tura ƴan sanda 4200 gabanin zanga-zangar da za a gudanar a cikin watan Agusta. Kamar yadda masu shirya...

Kamfanin NNPC ya shirya daukar karin ma’aikata

Kamfanin mai na Nigerian National Petroleum Company Limited ya shirya daukar karin ma’aikata.Kakakin kamfanin na NNPC, Olufemi Soneye, ya tabbatar da hakan a wata...

Ya kamata matasa su yi haƙuri zanga-zanga ba ita ce mafita ba – Sarkin Zazzau

Sarkin Zazzau, Mai Martaba Ahmed Nuhu Bamalli ya ce matasa su ƙara haƙuri da gwamnatin tarayya su janye zanga-zangar da suka shirya gudanarwa a...

Zanga-zanga: Tinubu ya gana da gwamnonin APC

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya gana da gwamnonin da aka zaɓa ƙarƙashin jam'iyar APC. Taron ganawar da aka gudanar a fadar shugaban ƙasa ta...