Ƴan sanda a Kano sun kama wani ɗan daba da ya kashe wani matashi

Jami’an ƴan sanda a jihar Kano, sun samu nasarar kama wani ɗan daba da ya kashe wani matashi a unguwar Dorayi dake birnin Kano.

Matashin mai suna Abba Garba wanda aka fi sani da Ɗan Ƙuda dake zaune a unguwar Ɗorayi Chiranchi ana zarginsa da  kashe wani matashi mai suna, Zahraddeen Iliyasu ta hanyar caka masa wuƙa a wuya bayan da suka samu saɓani.

Kakakin rundunar ƴan sandan jihar Kano, Abdullahi Haruna Kiyawa shi ne ya bayyana haka cikin wata sanarwa da ya fitar ranar Asabar.

Ya ce an kama matashin ne lokacin da yake ƙoƙarin tserewa ya zuwa ƙasar Jamhuriyar Nijar.

More News

Zanga-zanga: An jibge ƴan sanda 4200 a Abuja

Rundunar ƴan sandan birnin tarayya Abuja ta tura ƴan sanda 4200 gabanin zanga-zangar da za a gudanar a cikin watan Agusta. Kamar yadda masu shirya...

Kamfanin NNPC ya shirya daukar karin ma’aikata

Kamfanin mai na Nigerian National Petroleum Company Limited ya shirya daukar karin ma’aikata.Kakakin kamfanin na NNPC, Olufemi Soneye, ya tabbatar da hakan a wata...

Ya kamata matasa su yi haƙuri zanga-zanga ba ita ce mafita ba – Sarkin Zazzau

Sarkin Zazzau, Mai Martaba Ahmed Nuhu Bamalli ya ce matasa su ƙara haƙuri da gwamnatin tarayya su janye zanga-zangar da suka shirya gudanarwa a...

Zanga-zanga: Tinubu ya gana da gwamnonin APC

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya gana da gwamnonin da aka zaɓa ƙarƙashin jam'iyar APC. Taron ganawar da aka gudanar a fadar shugaban ƙasa ta...