Zulum Ya ziyarci wasu gonaki dake Jere, Mafa da Dikwa

Gwamnan jihar Borno, Babagana Umara Zulum a ranar Laraba, ya ziyarci wasu gonaki 10 dake kananan hukumomin hudu a wajen birnin Maiduguri.

Kananan hukumomin sun hada da Maiduguri Metropolitan Council, Mafa, Jere da kumma Difa.

A yayin ziyarar ta bazata Zulum wanda farfesa ne a harkar noman rani ya tattauna da manoman inda ya tambaye su matsaloloin da suke fuskanta domin magance su.

Yawancin gonakin da gwamnan ya ziyarta ya iske manomansu suna nome ciyawa.

Zulum ya yiwa manoman bayani cewa ba kamar sauran jihohi ba jihar Borno bata iya sawo taki ba domin rabawa manoma saboda hani da aka yi daga ofishin mai bada shawara akan harkar tsaro duba da yadda yan taadda ke amfani da shi wajen hada bama-bamai.

Saboda hanin da aka yi zabin da ya rage musu kawai shi ne yin am amfani da taki na ruwa.

More News

Yan bindiga sun harbi dalibai uku a Nasarawa

Dalibai uku na kwalejin kimiya da fasaha ta jihar Nasarawa ne suka jikkata a wani hari da yan bindiga suka kai. Mai magana da yawun...

Gobara ta kama wani sashe na kotun ƙolin Najeriya

An samu tashin gobara a wani sashe na Kotun Kolin Najeriya dake birnin tarayya Abuja. Kawo yanzu babu wani bayani kan musabbabin tashin gobarar amma...

Yan bindiga sun sace kwamishinan yaÉ—a labarai na Benue

Yan bindiga sun yi garkuwa da, Matthew Abo Kwamishinan Yada Labarai, Al'adu da Yawon Bude Ido na jihar Benue. An yi garkuwa da Abo a...

Nan bada jimawa za a kawo karshen rashin wutar lantarki a Kebbi

Gwamnatin jihar Kebbi ta roki mazauna jihar da su kara hakuri inda ta ce rashin wutar lantarki da ake fuskanta a jihar zai zo...