Zulum Ya ziyarci wasu gonaki dake Jere, Mafa da Dikwa

Gwamnan jihar Borno, Babagana Umara Zulum a ranar Laraba, ya ziyarci wasu gonaki 10 dake kananan hukumomin hudu a wajen birnin Maiduguri.

Kananan hukumomin sun hada da Maiduguri Metropolitan Council, Mafa, Jere da kumma Difa.

A yayin ziyarar ta bazata Zulum wanda farfesa ne a harkar noman rani ya tattauna da manoman inda ya tambaye su matsaloloin da suke fuskanta domin magance su.

Yawancin gonakin da gwamnan ya ziyarta ya iske manomansu suna nome ciyawa.

Zulum ya yiwa manoman bayani cewa ba kamar sauran jihohi ba jihar Borno bata iya sawo taki ba domin rabawa manoma saboda hani da aka yi daga ofishin mai bada shawara akan harkar tsaro duba da yadda yan taadda ke amfani da shi wajen hada bama-bamai.

Saboda hanin da aka yi zabin da ya rage musu kawai shi ne yin am amfani da taki na ruwa.

More News

Yahaya Bello Ya Bayyana Dalilan Da Ya Hana Shi Bayyana A Gaban Kotu

Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya ce tsoron kamun  hukumar EFCC dake yaÆ™i da yiwa tattalin arzikin Æ™asa ne ya hana shi bayyana...

Ƴan sanda sun kama mutane biyu dake samarwa ƴan fashin daji makamai a jihar Kaduna

Rundunar Æ´an sandan jihar Kaduna ta ce tana tsare da wasu mutane biyu da ake zargi da safarar bindiga a jihar. A wata sanarwa ranar...

An kori sojojin Najeriya biyu saboda satar kebul a matatar Dangote

Rundunar sojin Najeriya ta tabbatar da korar wasu sojoji biyu da ake zargi da satar igiyoyin sulke a harabar matatar Dangote da ke jihar...

Magoya bayan APC da dama sun koma NNPP a Kano

Jam'iyar NNPP ta karɓi magoya bayan jam'iyar APC da dama a jihar Kano. Mataimakin gwamnan jihar Kano, Aminu Abdul Salam Gwarzo shi ne ya karɓi...