Zulum Ya ziyarci wasu gonaki dake Jere, Mafa da Dikwa

Gwamnan jihar Borno, Babagana Umara Zulum a ranar Laraba, ya ziyarci wasu gonaki 10 dake kananan hukumomin hudu a wajen birnin Maiduguri.

Kananan hukumomin sun hada da Maiduguri Metropolitan Council, Mafa, Jere da kumma Difa.

A yayin ziyarar ta bazata Zulum wanda farfesa ne a harkar noman rani ya tattauna da manoman inda ya tambaye su matsaloloin da suke fuskanta domin magance su.

Yawancin gonakin da gwamnan ya ziyarta ya iske manomansu suna nome ciyawa.

Zulum ya yiwa manoman bayani cewa ba kamar sauran jihohi ba jihar Borno bata iya sawo taki ba domin rabawa manoma saboda hani da aka yi daga ofishin mai bada shawara akan harkar tsaro duba da yadda yan taadda ke amfani da shi wajen hada bama-bamai.

Saboda hanin da aka yi zabin da ya rage musu kawai shi ne yin am amfani da taki na ruwa.

More News

MTN yana ƙoƙarin ƙara kuɗin kati da data a Najeriya

Katafaren kamfanin sadarwa na MTN na kokarin kara kudin katin waya da na data a Najeriya. Kamfanin sadarwa mafi girma a nahiyar Afirka ya ba...

Gwamnatin Kano Ta Rage ₦500,000 A Kuɗin Aikin Hajjin Bana

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya sanar da yiwa maniyatan Aikin Hajji da suka fito daga jihar kyautar ₦500,000 domin su cika kuɗin...

Ƴan bindiga sun sace wani limami a jihar Kogi

Ƴan bindiga sun yi garkuwa da Quasim Musa babban limamin garin Iyara dake ƙaramar hukumar Ijumu ta jihar Kogi. Lamarin ya faru ne a ranar...

Delta: An dawo da gawarwakin sojojin da aka kashe Abuja don yi musu jana’iza

Gawarwakin sojojin da aka kashe a jihar Delta kwanan nan sun isa maƙabartar sojoji ta kasa da ke Abuja. Gawarwakin sun iso ne da misalin...