Zulum ya yi wa ma’aikatan lafiya a Borno Ć™arin albashi mai tsoka

Gwamna Babagana Umar Zulum na jihar Borno ya ce ma’aikatan lafiya da suka amince su yi aiki a karkara za su samu karin kashi 30 cikin 100 na albashin da suke karba a yanzu.

Gwamnan ya bayyana hakan ne a wajen kaddamar da rabon tallafin N100,000 da kayan abinci ga tsofaffi (shekaru 65 zuwa sama) a karkashin kungiyar Renewed Hope Initiative na uwargidan shugaban kasar, Oluremi Tinubu.

Ya ce matakin kuma na daga cikin shirin gwamnatinsa na tallafa wa tsofaffi ta kowace hanya, inda ya ce jihar za ta samar da likitocin da suka kware wajen kula da tsofaffi a cibiyoyin kiwon lafiya a fadin jihar.

Zulum, wanda ya samu wakilcin kwamishinan lafiya, Farfesa Baba Malam Gana, ya bayyana cewa nan ba da jimawa ba za a kafa sashen kula da tsofaffi a asibitin koyarwa na jami’ar jihar Borno da ke Maiduguri.

More News

Gwamantin Kano na kashe naira biliyan 1.2 duk wata don samar da ruwan sha—Kwamishina

Gwamnatin jihar Kano na kashe kimanin naira biliyan 1.2 duk wata don samar da ruwan sha na tafi da gidanka a cikin babban birnin...

Wasu É—aliban Jami’ar Jihar Nasarawa sun mutu a lokacin turmutsutsin karÉ“ar tallafin abinci

Dalibai biyu daga Jami’ar Jihar Nasarawa da ke Keffi (NSUK) sun rasa rayukansu a wani turmutsitsi da ya barke a lokacin da suke kokarin...

Jarumin Nollywwood, Mr. Ibu, ya rasu

Jarumin Nollywood, John Okafor, wanda aka fi sani da "Mr Ibu", ya rasu yana da shekaru 62. Emeka Rollas, shugaban kungiyar Actors Guild of Nigeria,...

Miyetti Allah ta nemi a cafke Sunday Igboho saboda barazanar yaƙar Fulani

Kungiyar Miyetti Allah Cattle Breeders Association of Nigeria, MACBAN, ta yi kira da a damke wani dan kabilar Yarbawa, Sunday Adeyemo, wanda aka fi...