Zulum ya yi wa ma’aikatan lafiya a Borno ƙarin albashi mai tsoka

Gwamna Babagana Umar Zulum na jihar Borno ya ce ma’aikatan lafiya da suka amince su yi aiki a karkara za su samu karin kashi 30 cikin 100 na albashin da suke karba a yanzu.

Gwamnan ya bayyana hakan ne a wajen kaddamar da rabon tallafin N100,000 da kayan abinci ga tsofaffi (shekaru 65 zuwa sama) a karkashin kungiyar Renewed Hope Initiative na uwargidan shugaban kasar, Oluremi Tinubu.

Ya ce matakin kuma na daga cikin shirin gwamnatinsa na tallafa wa tsofaffi ta kowace hanya, inda ya ce jihar za ta samar da likitocin da suka kware wajen kula da tsofaffi a cibiyoyin kiwon lafiya a fadin jihar.

Zulum, wanda ya samu wakilcin kwamishinan lafiya, Farfesa Baba Malam Gana, ya bayyana cewa nan ba da jimawa ba za a kafa sashen kula da tsofaffi a asibitin koyarwa na jami’ar jihar Borno da ke Maiduguri.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]