Zanga-zanga:Matasa garin Suleja sun rufe hanyar Abuja zuwa Kaduna 

Wasu matasa sun fantsama kan tituna inda suke zanga-zanga kan tsananin matsin rayuwa da ake fama da shi a ƙasarnan.

Zanga-zangar ta su na zuwa ne kwanaki biyu gabanin fara zanga-zangar da aka shirya farawa a ranar 1 ga watan Agusta.

Amma kuma wasu matasa a garin Suleja dake jihar Niger sun yi riga malam masallaci inda suka fantsama kan tituna ɗauke da kwalaye da aka rubuta “Dole a dawo da tallafin mai” ” Ya isa haka ya isa haka” ” Mu ba bayi bane ƙasarmu” da sauran rubututtuka makamantan haka.

Masu zanga-zangar na jerin gwano ne akan babbar hanyar Abuja-Kaduna ta ratsa garin na Suleja inda suke faɗin kalaman nuna ƙin jinin gwamnati.

Gwamnonin jihohi da kuma shugaban ƙasa sun yi kiraye-kiraye ga matasa da su janye batun zanga-zangar da suke shirin gudanarwa.

Suma jami’an tsaro sun gargadi masu shirya-shirya zanga-zangar cewa wasu ɓata gari ka iya amfani da damar wajen tayar da zaune tsaye.

More from this stream

Recomended