Zanga-zanga: Tinubu ya gana da gwamnonin APC

Shugaban Æ™asa, Bola Ahmad Tinubu ya gana da gwamnonin da aka zaÉ“a Æ™arÆ™ashin jam’iyar APC.

Taron ganawar da aka gudanar a fadar shugaban ƙasa ta Aso Rock dake Abuja na zuwa ne ƴan kwanaki kaɗan gabanin  fara zanga-zangar ƙasa baki ɗaya da aka shirya gudanarwa saboda matsin tattalin arziki dake addabar mutane.

Cire tallafin man fetur da kuma dai-daita farashin kasuwar canjin kuɗaɗen ƙasar waje ta haifar da mummunan tashin farashin kayayyaki.

Akwai rahotannin dake cewa zanga-zangar zata fara ne a makon farko na watan Agusta.

Hope Uzodimma gwamnan jihar Imo da kuma gwamnan jihar Kwara shugaban ƙungiyar gwamnonin APC, Abdurrahaman Abdulrazak su ne suka yiwa gwamonin jagora ya zuwa fadar ta Aso Rock.

Akwai dai kiraye-kiraye daga bangarori da dama dake kiran da ajanye batun zanga-zangar saboda gudun kada É“atagari su shiga ciki.

More News

Mai magana da yawun Tinubu ya ajiye aikinsa na wani lokaci

Mai ba shugaban kasa shawara na musamman kan harkokin yada labarai Ajuri Ngelale ya ajiye aikinsa na wani lokaci domin tunkarar matsalar lafiya.Mista Ngelale...

Ali Jita ya koma jam’iyar APC daga NNPP

Mataimakin shugaban majalisar dattawa dattawa, Sanata Barau Jibrin ya karɓi fitaccen mawakin Kannywood, Aliyu Isa Jita daga jam'iyar NNPP ya zuwa jam'iyar APC. Ali Jita...

An yi jana’izar mutumin da ya Æ™irÆ™iri tutar Najeriya

Iyalan marigayi, Pa Taiwo Akinkumi mutumin da ya ƙirƙiro tutar Najeriya sun yi bikin binne shi bayan da gwamnatin tarayya ta gaza cika alƙawarin...

‘Za a Æ™ara wa Æ´an bautar Æ™asa na NYSC alawus’

Babban daraktan hukumar yi wa kasa hidima ta kasa (NYSC) Birgediya Janar Yushau Ahmed, ya tabbatar wa ‘yan bautar kasar cewa za a kara...