Zan Kawo Sauyi A Jihar Filato – Simon Lalong

Bayan rantsuwar kama aiki da gwamnan jahar Filato Simon Lalong ya yi na ci gaba da shugabancin jihar karo na biyu, wasu al’ummar jihar sun bayyana fatar samun sauyi masu inganci da zasu kyautata rayuwar su.

Babban batu da yafi dauke hankalin mutane Filato shine batun baiwa matsa aiki yi domin dogaro da kai. Sai batun batun ilimi da inganta karatu ta yanda matasa ba zasu dogara da ayyukan gwamnati ba, su iya kafa sana’o’i domin taimakawa kawunan su kuma hakan zai sa a samu saukin tashe tashen hankula a jihar.

Shiko gwamnan jihar Filato, a hira sa da Muryar Amurka a kwanakin baya, ya yi bayani a kan abubuwan da zai fuskanta a mulkin sa karo na biyu, da suka hada da biyan albashin ma’aikata da samar da tsaro ga al’ummar jihar.

Shima gwamnan jihar Jigawa Muhammad Badaru Abubakar wanda ma’abucin jihar Pilato ne yace yana da yakinin Simon Lalong zai samar da sauye-sauye masu inganci a jahar.

More News

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miÆ™ata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...

An dakatar da ayyukan kamfanin jiragen sama na Dana Air

Festus Keyamo, ministan harkokin sufurin jiragen sama ya umarci hukumar FAAN dake lura da sufurin jiragen sama a Najeriya ta dakatar da ayyukan kamfanin...

Yahaya Bello Ya Bayyana Dalilan Da Ya Hana Shi Bayyana A Gaban Kotu

Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya ce tsoron kamun  hukumar EFCC dake yaÆ™i da yiwa tattalin arzikin Æ™asa ne ya hana shi bayyana...

Ƴan sanda sun kama mutane biyu dake samarwa ƴan fashin daji makamai a jihar Kaduna

Rundunar Æ´an sandan jihar Kaduna ta ce tana tsare da wasu mutane biyu da ake zargi da safarar bindiga a jihar. A wata sanarwa ranar...