Zan Kawo Sauyi A Jihar Filato – Simon Lalong

Bayan rantsuwar kama aiki da gwamnan jahar Filato Simon Lalong ya yi na ci gaba da shugabancin jihar karo na biyu, wasu al’ummar jihar sun bayyana fatar samun sauyi masu inganci da zasu kyautata rayuwar su.

Babban batu da yafi dauke hankalin mutane Filato shine batun baiwa matsa aiki yi domin dogaro da kai. Sai batun batun ilimi da inganta karatu ta yanda matasa ba zasu dogara da ayyukan gwamnati ba, su iya kafa sana’o’i domin taimakawa kawunan su kuma hakan zai sa a samu saukin tashe tashen hankula a jihar.

Shiko gwamnan jihar Filato, a hira sa da Muryar Amurka a kwanakin baya, ya yi bayani a kan abubuwan da zai fuskanta a mulkin sa karo na biyu, da suka hada da biyan albashin ma’aikata da samar da tsaro ga al’ummar jihar.

Shima gwamnan jihar Jigawa Muhammad Badaru Abubakar wanda ma’abucin jihar Pilato ne yace yana da yakinin Simon Lalong zai samar da sauye-sauye masu inganci a jahar.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan YaÆ™i Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin Æ™wazon jagorancinsa wajen yaÆ™i da ta’addanci da magance matsalar tsaro a Æ™asar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiÆ™a da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]