Zakzaky ya gargadi Tinubu game da kai hari Jamhuriyar Nijar

Jagoran Harkar Musulunci a Najeriya, Ibrahim El-Zakzaky ya gargadi Shugaba Bola Tinubu kan kai wa Jamhuriyar Nijar hari.

El-Zakzaky ya yi zargin cewa Faransa da Amurka, na kokarin amfani da Najeriya wajen kai wa Jamhuriyar Nijar hari.

Ya ce kamata ya yi Tinubu ya fahimci cewa Nijeriya da Jamhuriyar Nijar abu daya ne idan aka duba tarihi, yana mai cewa irin wannan matakin abin mamaki ne.

Ya jaddada cewa kamata ya yi Tinubu ya sake duba shirin kai hari a Jamhuriyar Nijar.

A cikin wata sanarwa da ya sanya wa hannu, El-Zakzaky ya gano hadin kan da ke tsakanin Najeriya da Nijar a tarihi.

A cewarsa: “Ba zato ba tsammani, Faransa da Amurka suna so su yi amfani da Najeriya su kai wa Nijar hari.

“Wannan abu ne mai ban mamaki idan aka yi la’akari da cewa Najeriya da Nijar mutane daya ne.

“Masarautu ne aka aka sassaka don haifar da Nijar da Najeriya.”

A ranar Talata ne gwamnatin Nijar ta ki amincewa da sabuwar tawagar diflomasiyya daga kasashen Afirka.

More News

Tsoffin gwamnoni sun wawashe sama da naira tiriliyan 2 tun komawa dimokuraÉ—iyya

Aƙalla tsoffin gwamnoni 58 ne ake zargin sun wawure kuma sun yi almubazzarancin jimillar naira Tiriliyan 2.187 a cikin shekaru 25 tun komawa mulkin...

Ƴan sanda sun kama mutane 50 kan rikicin da ya faru a wata kasuwa a Lagos

Rundunar Æ´an sandan jihar Legas ta kama mutane sama da 50 da ake zargin suna da hannu rikicin da ya faru a kasuwar Ile...

Ƴan Sanda sun kama wanda ya shirya kai harin jirgin ƙasar Abuja-Kaduna a shekarar 2022

Rundunar ƴan sandan Najeriya ta ce jami'anta sun kama wani mutum mai suna Ibrahim Abdullahi wanda ake zargi da kitsa harin jirgin ƙasar da...

Ƴansanda sun kama wanda ya kitsa harin da aka kai wa jirgin ƙasa a Kaduna

Rundunar ‘yan sandan Najeriya a ranar Alhamis, ta sanar da kame wanda ake zargin ya shirya harin da aka kai a jirgin ƙasan Abuja-Kaduna...