Hakkin mallakar hoto
Reuters
Zakaran da aka maka a kotu a kasar Faransa ya yi nasara bayan da kotun ta kammala shai’ar kararsa da aka kai cewa yana damun makwabta da cara.
An zargi zakaran mai suna Maurice wanda yake rayuwarsa da kiwo a yankin Oleron da ke gabar Tekun Atlantika ne da laifin damun wasu dattijan ma’aurata biyu da ke makwabtaka da shi, sakamakon carar da yake yi da asubahin fari.
Labarin carar Maurice ya karade kasashe da dama a duniya inda ya samu dumbin magoya baya.
Mai Zakaran, Corinne Fesseau ta nuna farin ciki matuka da jin hukuncin da kotun ta yanke.
Ta ce wannan babban nasara ce ga kowa da ke cikin “irin wannan hali kamar ni,” kuma ta yi fatan ya zame wa sauran mutane izina.
A wani zama da aka yi a kotu a watan Yuli, lauyanta ya ce shigar da karar almara ce saboda carar zakaru dabi’a ce ta rayuwa.
Da an samu akasin yin nasara, to da Madam Fesseau, wacce ta kwashe shekara 35 tana rayuwarta a yankin Oleron ta sauya wuri ko kuma ta san yadda za ta yi ta hana Maurice yin cara.
Sai dai a yanzu da ta yi nasara, lauyanta a ranar Alhamis ya ce, yanzu ita za a bai wa Euro 1000 na neman bata mata suna da aka yi, kwatankwacin naira 400,000.
Hakkin mallakar hoto
Reuters
Ms Fesseau ta yi kokarin hana shi yin cara – har da rufe masa baki da takarda
Wannan lamari ya jawo an kaddamar da korafi a intanet inda mutum 140,000 suka sanya wa hannu.
Zakaran mai shekara hudu ya zama wani fitacce a Faransa, inda ya zama daya daga cikin abubuwan tunkaho na kasar.
An yi ta samar da abubuwa da nufin girmama shi tare da aika wasikun goyon baya daga kasashe daban-daban ciki har da Amurka, a cewar kamfanin dillancin labarai na Reuters.
Ana danganta wannan gagarumin lamari da irin tashin hankalin da ke karuwa tsakanin mazauna yankunan karkara a Faransa da kuma masu guduwa birane don yin rayuwa.
Wani magajin gari kauyensu Madan Fessau, Christophe Sueur, ya shaida wa kamfanin dillancin labarai na AFP cewa, “Wannan abu ne da ba za a yarda da shi ba – dole ne a rungumi al’adun gargajiya.”
Haka ma magajin wani garin daban, Bruno Dionis du Sejour, ya rubuta budaddiyar wasika a watan Mayu, yana kira cewa, “Ya kamata a sanya koke-koken dabbobi irin su shanu da kuma kararrawar coci a jerin abubuwan al’adu na kasar domin ba su kariya ko da irin hakan ya faru.