Zaben Amurka na 2020: Shin masu fafutukar Black Lives Matter za su iya tasiri a zaben kasar?
Masu fafutukar kare hakkin bakaken fata da ake yi wa lakabi da Black Lives Matter sun kwashe tsawon lokaci suna hankoron ganin an kare martabar bakar fata a Amurka.
Fafutukarsu ta samu karbuwa sosai bayan kisan da ‘yan sandan kasar suka yi wa wani bakar fata da baya dauke da makami, Mr George Floyd.
Hakan ya harzuka mutane da dama a kasashen duniya inda aka rika gudanar da jerin gangami a birane daban-daban na duniya.
Sai dai wasu ‘yan siyasa irin su Shugaba Donald Trump sun bayyana kungiyar a matsayin ta ‘yan ta’adda.
Amma duk da haka wasu da ke fafutuka cikin ta sun tsaya zabuka kuma sun yi nasara.
Shin wannan fafutuka za ta iya yin tasiri a kan sakamakkon zaben kasar na 2020?