Za mu taimaka wa Falasɗinawa a yaƙinsu da Isra’ila—Hezbollah

Mataimakin shugaban ƙungiyar Hezbollah ya yi fatal da kiraye-kirayen da ake masu na kada su shiga yaƙin da ake gwabzawa tsakanin Gaza da Isra’ila.

A cewar Na’im Qassem, ƙungiyarsu a shirye take don yaƙar Isra’ila idan akwai bukatar hakan.

Ko satin da ya gabata ƙungiyar Hezbollah ta gwabza rikici da dakarun Isra’ila a kan iyakar Labanon.

Kalaman na ƙungiyar sun zo daidai lokacin da ministan harkokin wajen Iran ya kai ziyara a birnin Beirut.

Tehran na ba da tallafin kuɗi da na soji ga Hizbullah.

More News

Gwamantin Kano na kashe naira biliyan 1.2 duk wata don samar da ruwan sha—Kwamishina

Gwamnatin jihar Kano na kashe kimanin naira biliyan 1.2 duk wata don samar da ruwan sha na tafi da gidanka a cikin babban birnin...

Wasu ɗaliban Jami’ar Jihar Nasarawa sun mutu a lokacin turmutsutsin karɓar tallafin abinci

Dalibai biyu daga Jami’ar Jihar Nasarawa da ke Keffi (NSUK) sun rasa rayukansu a wani turmutsitsi da ya barke a lokacin da suke kokarin...

Jarumin Nollywwood, Mr. Ibu, ya rasu

Jarumin Nollywood, John Okafor, wanda aka fi sani da "Mr Ibu", ya rasu yana da shekaru 62. Emeka Rollas, shugaban kungiyar Actors Guild of Nigeria,...

Miyetti Allah ta nemi a cafke Sunday Igboho saboda barazanar yaƙar Fulani

Kungiyar Miyetti Allah Cattle Breeders Association of Nigeria, MACBAN, ta yi kira da a damke wani dan kabilar Yarbawa, Sunday Adeyemo, wanda aka fi...