Za mu taimaka wa Falasɗinawa a yaƙinsu da Isra’ila—Hezbollah

Mataimakin shugaban ƙungiyar Hezbollah ya yi fatal da kiraye-kirayen da ake masu na kada su shiga yaƙin da ake gwabzawa tsakanin Gaza da Isra’ila.

A cewar Na’im Qassem, ƙungiyarsu a shirye take don yaƙar Isra’ila idan akwai bukatar hakan.

Ko satin da ya gabata ƙungiyar Hezbollah ta gwabza rikici da dakarun Isra’ila a kan iyakar Labanon.

Kalaman na ƙungiyar sun zo daidai lokacin da ministan harkokin wajen Iran ya kai ziyara a birnin Beirut.

Tehran na ba da tallafin kuɗi da na soji ga Hizbullah.

More from this stream

Recomended