Za mu dauki mataki kan jifar shugabanninmu a Ogun – APC

Shugaba Muhammadu Buhari

Hakkin mallakar hoto
Getty Images

Jam’iyyar APC mai mulki a Najeriya ta nuna rashin jin dadinta kan yadda aka jefi shugabanninta a gangamin yakin neman zaben shugaba Buhari a jihar Ogun.

Wata sanarwa da jam’iyyar ta fitar ta ce za ta dauki mataki kan gwamnan jihar Ibikunle Amosun wanda ta zarga da shirya cin mutuncin ga shugabanta Adams Oshiomhole a gaban idon shugaba Buhari.

A ranar Litinin ne wasu suka jefi Adams Oshiomhole a yayin da shugaba Muhammadu Buhari ke gangamin zabensa a birnin Abeokuta.

An jefi Oshiomhole ne bayan da ya ambaci sunan dan takarar gwamna na APC a jihar, Mista Dapo Abiodun wanda gwamnan jihar ba ya goyon baya, matakin da ya harzuka mutanen da suka halarci gangamin.

APC ta ce ba za ta lamunce wa wannan rashin da’a ba daga duk wani mambanta.

Ta ce za ta yi nazari kan abin da ya faru inda aka kunyata Buhari da shugabanninta kuma za ta dauki mataki akai bayan an kammala zabe.

Lamarin ya kai sai da jam’ian tsaro suka rika kare shugaba Buharir daga masu jifa kafin kammala taron.

More News

Yawan Mutanen Da Suka Mutu A Wutar Da Wani Matashi Ya Cinnawa Wani Masallaci A Kano Sun  Karu Zuwa 16

Rundunar ƴan sandan jihar Kano ta ce yawan mutanen da suka mutu sakamakon wutar da wani ya cinnawa wani masallaci a ƙauyen Gadan a...

An fara rushe wasu gine-gine 500 a kasuwar Karmo dake Abuja

Hukumar FCTA dake kula da birnin tarayya Abuja ta fara rushe gine-gine sama da 500 da aka yi ba bisa ka'ida ba a kasuwar...

Tinubu ya tarbi shugaban kasar Senegal Bassirou Faye a fadar Aso Rock Villa

A ranar Alhamis ne shugaba Bola Tinubu ya tarbi shugaban kasar Senegal Bassirou Faye a fadar Aso Rock Villa, a ziyarar da Faye ya...

NEMA ta karɓi ƴan Najeriya 150 da aka dawo dasu gida daga ƙasar Chad

Hukumar Bada Agajin Gaggawa ta Ƙasa NEMA ta ce ta karɓi ƴan Najeriya 150 da aka dawo da su bayan da su ka maƙale...