An fara rushe wasu gine-gine 500 a kasuwar Karmo dake Abuja

Hukumar FCTA dake kula da birnin tarayya Abuja ta fara rushe gine-gine sama da 500 da aka yi ba bisa ka’ida ba a kasuwar Karmo dake Abuja.

Mukhtar Galadima daraktan sashen dake kare birnin daga bunÆ™asa ba tare da tsari ba ya ce an fara rushe-rushen ne biyo bayan Æ™arewar wa’adin awanni 24 da aka bawa Æ´an kasuwar na su tashi daga wurin.

Galadima wanda ya samu wakilcin Garba Jibril mataimakin darakta dake lura da yankin Karmo da sauran wasu yankuna ya ce an sanar da dukkan mutanen da abun ya shafa inda ya Æ™ara da cewa anbi dukkanin wata ka’ida kafin a fara aikin.

“A fili yake Æ™arara mutane suna shafe a wanni kafin su wuce ta titin  musamman ranar da kasuwa take ci,” ya ce.

“Domin shawo kan wannan matsalar ministan Abuja Nyesom Wike ya bayar da umarnin rushe gine-gine da aka yi ba bisa ka’ida ba,” ya ce.

Galadima ya yi kira ga Æ´an kasuwar da abun ya shafa da su koma kasuwannin da aka samar .

More News

Zanga-zanga: An jibge Æ´an sanda 4200 a Abuja

Rundunar Æ´an sandan birnin tarayya Abuja ta tura Æ´an sanda 4200 gabanin zanga-zangar da za a gudanar a cikin watan Agusta. Kamar yadda masu shirya...

Kamfanin NNPC ya shirya daukar karin ma’aikata

Kamfanin mai na Nigerian National Petroleum Company Limited ya shirya daukar karin ma’aikata.Kakakin kamfanin na NNPC, Olufemi Soneye, ya tabbatar da hakan a wata...

Ya kamata matasa su yi haÆ™uri zanga-zanga ba ita ce mafita ba – Sarkin Zazzau

Sarkin Zazzau, Mai Martaba Ahmed Nuhu Bamalli ya ce matasa su ƙara haƙuri da gwamnatin tarayya su janye zanga-zangar da suka shirya gudanarwa a...

Zanga-zanga: Tinubu ya gana da gwamnonin APC

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya gana da gwamnonin da aka zaɓa ƙarƙashin jam'iyar APC. Taron ganawar da aka gudanar a fadar shugaban ƙasa ta...