Ma’aikatan fannin wutar lantarki sun bi sahun kungiyar kwadago ta kasa NLC a yajin aikin gargadin da ta fara kan tasirin da cire tallafin man fetur ya yi akan yan Najeriya.
A ranar 1 ga watan Satumba ne kungiyar NLC ta sanar da shirin fara yajin aikin gargadi na kwanaki biyu bayan da ta zargi gwamnatin tarayya da yin watsi da tattaunawar da ake.
Kungiyar ta ce gwamnatin ta gaza aiwatar da wasu daga cikin alkawuran da aka cimma a tarukan ganawar da aka yi a baya.
A wani abu na nuna goyon baya ga kungiyar ta NLC kamfanonin rarraba hasken wutar lantarki a ranar Talata sun sanar cewa sun shiga yajin aikin.