‘Yar autan Nelson Mandela Zindzi ta mutu tana da shekara 59

Zindzi Mandela

Hakkin mallakar hoto
Getty Images

Zindzi Mandela, ƴar Nelson Mandela da Winnie Madikizela-Mandela, wadanda suka sadaukar da rayukansu domin yaƙar tsarin nuna bambancin launin fata ta mutu kamar yadda tashar SABC ta gwamnatin Afirka ta Kudu ta ruwaito.

Ta mutu a birnin Johannesburg ranar Litinin tana da shekara 59.

Wani É—an uwanta ya tabbatar da mutuwarta, in ji tashar ta SABC.

Ita ce jakadiyar Afirka ta Kudu a Denmark a lokacin da ta mutu, amma ba a bayyana abin da yayi sanadin mutuwarta ba.

Wani rahoto da tashar SABC tayi na cewa, “Ƴar tsohon shugaba Nelson Mandela da tsohuwar mai gwagwarmayar samar da Æ´anci Winnie Madikizela-Mandela ta mutu a wani asibitin Johannesburgda sanyin safiyar nan.”

Ita ce Æ´ar Nelson Mandela ta shida kuma ta biyu da ya samu tare da Winnie Madikizela-Mandela.

More News

Gwamnan Kano ya sanya hannu kan dokar yin gwajin lafiya kafin aure

Gwamnan jihar Kano, Engr Abba Kabir Yusuf ya sanya hannu kan wata doka za ta tilastawa masu yin aure yin wasu gwaje-gwajen lafiya gabanin...

An kashe kwamandan soji a Katsina

An kashe kwamandan sojoji na wani sansanin soji da ke Sabon Garin Dan’Ali a karamar hukumar Danmusa a jihar Katsina a wani harin kwantan...

Magoya bayan APC da dama sun koma NNPP a Kano

Jam'iyar NNPP ta karɓi magoya bayan jam'iyar APC da dama a jihar Kano. Mataimakin gwamnan jihar Kano, Aminu Abdul Salam Gwarzo shi ne ya karɓi...

APC ta dakatar da Ganduje a matakin gunduma

Mambobin jam'iyyar APC a mazabar da ke Karamar Hukumar Dawakin Tofa a Jihar Kano sun dakatar da Shugaban Jam’iyyar APC na kasa Abdullahi Ganduje. ...