Yankin arewa maso gabas zai fuskanci daukewar wutar lantarki na kwanaki 4

Kamfanin TCN dake dakon wutar lantarki a Najeriya ya sanar da kamfanonin rarraba hasken wutar lantarki a jihohi  6 na yankin arewa maso gabas cewa za a fuskanci daukewar wutar lantarki a yankin a yayin da a wasu wuraren za a fuskanci karancin samun wutar lantarki.

A wata wasika da aka turawa daya  daga cikin kamfanonin rarraba hasken wutar lantarkin a shiyar mai dauke da sahannun manajan TCN na ayyukan yau da kullum, Engr J.O Joseph ya ce za a samu raguwar wutar da ake turowa yankin saboda za a kafa turakun wuta mai karfin 330kV a karamar tashar rarraba wutar lantarki dake Bauchi.

Sanarwar ta ce za a fuskanci daukewar wutar lantarkin daga ranar 10 ya zuwa ranar 14 ga watan Yuni kuma zai shafi babban layin da ya taso daga Jos-Bauchi-Gombe mai karfin 132kV.

Da yake tabbatar da labarin kamfanin rarraba hasken wutar lantarki na Yola ya ce daukewar wutar zai shafi wani bangaren na jihohin Adamawa, Borno, Yobe da kuma Taraba.

More from this stream

Recomended