Yan shi’a sun gudanar da zanga-zanga inda suka nemi yan Najeriya su mayar da Buhari Daura

Mambobin kungiyar yan uwa musulmi da akafi sani da yan shi’a da suka fito daga yankin kudu maso yammacin kasarnan sun yi kira ga mutanen dake yankin da kada su zaɓi shugaban kasa Muhammad Buhari a zaben 2019.

Da sukewa yan jaridu jawabi a bakin kofar shiga fadar shugaban kasa ta Aso Rock dake Abuja a ranar Laraba,Muftau Zakariyya jami’in tsare-tsare na shiyar kudu maso gabas ya ce shugaban kasa Buhari bashi dalilin da zai sa ya cigaba da zama akan mulki bayan shekarar 2019.

Ƙungiyar ta zargi Buhari da yin mulkin kama karya inda ta ce baya mutunta doka da oda.

Ƙungiyar ta gudanar da jerin zanga-zanga na neman a sako jagoransu, Ibrahim Elzakzaky wanda ke tsare a hannu gwamnati tun shekarar 2015.

“Munzo ne yau muyi zanga-zanga neman a sako jihar jagoranmu da kuma mu shawo kan gwamnati da ta bi umarnin kotu,” ya ce.

Kotuna da dama ne suka bayar da belin shugaban kungiyar sai dai kuma kuma gwamnati ta cigaba da tsare shi

.

More News

Yawan Mutanen Da Suka Mutu A Wutar Da Wani Matashi Ya Cinnawa Wani Masallaci A Kano Sun  Karu Zuwa 16

Rundunar ƴan sandan jihar Kano ta ce yawan mutanen da suka mutu sakamakon wutar da wani ya cinnawa wani masallaci a ƙauyen Gadan a...

An fara rushe wasu gine-gine 500 a kasuwar Karmo dake Abuja

Hukumar FCTA dake kula da birnin tarayya Abuja ta fara rushe gine-gine sama da 500 da aka yi ba bisa ka'ida ba a kasuwar...

Tinubu ya tarbi shugaban kasar Senegal Bassirou Faye a fadar Aso Rock Villa

A ranar Alhamis ne shugaba Bola Tinubu ya tarbi shugaban kasar Senegal Bassirou Faye a fadar Aso Rock Villa, a ziyarar da Faye ya...

NEMA ta karɓi ƴan Najeriya 150 da aka dawo dasu gida daga ƙasar Chad

Hukumar Bada Agajin Gaggawa ta Ƙasa NEMA ta ce ta karɓi ƴan Najeriya 150 da aka dawo da su bayan da su ka maƙale...