Yan Sanda Sun Gano Shanu 4 Da Aka Sace A Gombe

Rundunar yan sandan jihar Gombe ta kwato wasu shanu hudu da ake zargin an sace su ne daga wasu gidajen mazauna a jihar ana gab da bikin Babbar Sallah.

Mai magana da yawun rundunar yan sandan jihar Mahid Mu’azu Abubakar shi ne ya bayyana haka cikin wata sanarwa da ya fitar ranar Alhamis.

A cewar sanarwar an gano biyu daga cikin shanun ne bayan da aka kai rahoton satar shanu ofishin yan sanda na Gona ranar Talata da misalin karfe 10:30 na dare.

Wani mutum mai suna Mallam Jibrin dake zaune a kauyen Gidim shi ne ya kai rahoton cewa wasu mutane sun shiga gidansa inda suka sace shanu da kudinsu ya kai dubu dari bakwai.

Bayan samun rahoton ne jami’an rundunar suka bazama inda suka gano shanun a wani gida da ba a kammala ba a unguwar Nassarawo, shanu hudu aka gano a gidan da ake zargin na sata ne kuma mutumin ya gane biyu daga ciki nasa ne da aka sace.

Har ila yau an gano wata karamar bindiga kirar gida a gidan ya yi da ake cigaba da bincike domin gano barayin da suka tsere.

More News

An fara rushe wasu gine-gine 500 a kasuwar Karmo dake Abuja

Hukumar FCTA dake kula da birnin tarayya Abuja ta fara rushe gine-gine sama da 500 da aka yi ba bisa ka'ida ba a kasuwar...

Tinubu ya tarbi shugaban kasar Senegal Bassirou Faye a fadar Aso Rock Villa

A ranar Alhamis ne shugaba Bola Tinubu ya tarbi shugaban kasar Senegal Bassirou Faye a fadar Aso Rock Villa, a ziyarar da Faye ya...

NEMA ta karɓi ƴan Najeriya 150 da aka dawo dasu gida daga ƙasar Chad

Hukumar Bada Agajin Gaggawa ta Ƙasa NEMA ta ce ta karɓi ƴan Najeriya 150 da aka dawo da su bayan da su ka maƙale...

Ƙungiyar ƙwadago ta ƙi amincewa da ₦48,000 a matsayin mafi ƙarancin albashi

Taron zaman ganawa da ƴan kungiyar ƙwadago da gwamnatin ta tarayya ta kira  ya tashi babu shiri bayan da wakilan kungiyar ƙwadago suka fice...