‘Yan sandan Neja sun ceto mutum 20 da ‘yan bindiaga suka yi garkuwa da su sakamakon samamen da suka kai kan sansanin ‘yan fashin daji a jihar da ke tsakiyar Najeriya.
Kakakin rundunar a Neja, DSP Wasiu A. Abiodun, ya faɗa cikin wata sanarwa ranar Lahadi cewa dakarunsu sun kai samamen ne a yankin Anaba da ke Ƙaramar Hukumar Magama.
Bayan fafatawa gami da harbe-harbe tare da ‘yan bindigar, dakaru sun yi nasarar kashe ‘yan fashin tare da Æ™wato shanun da suka sata.
“Ƙarin dakarun da aka tura ciki har da sojoji da ‘yan banga sun fara fafatawa da ‘yan bindigar a kan hanyar shanu da Ibeto kusan tsawon awa biyu a lokacin da maharan ke Æ™oÆ™arin guduwa,” in ji shi.
Daga cikin makaman da aka ƙwace daga hannunsu sun haɗa da bindigar AK-47 ɗaya da ƙunshin harsasai 30 da wayar salula bakwai da babur ɗaya, a cewar DSP Abiodun.