Yan sanda a jihar kebbi sun kama wani mutum da ya yiwa yarinya yar shekara 12 fyade

Rundunar yan sandan jihar Kebbi ta kama wani mutum mai suna Saidu Sani wanda aka fi sani da Dankahuwa kan laifin yiwa wata yarinya fyade mai suna Amina Isiya a karamar hukumar Aliero ta jihar.

A cewar yan sandan wani danuwan yarinyar ne mai suna Yushau Adamu ya kai rahoton faruwar lamarin wurin yan sanda.

Wanda ake zargi ya hilaci ƙaramar yarinyar zuwa ɗakinsa inda ya yi lalata da ita.

Mai magana da yawun rundunar yan sandan jihar, SP Nafiu Abubakar a cikin sanarwar da ya fitar ya ce wanda ake zargi bayan ya aikata fyade ya yi barazanar kashe yarinyar idan ta fadawa wani abun da ya faru.

Ya kara da cewa tuni aka shirya gurfanar da wanda ake zargin a gaban kotu.

More News

An samu ambaliyar ruwa a Adamawa

Anguwan Tana, al’ummar karamar hukumar Yola ta Arewa, sun shiga tasgaro a ranar Alhamis sakamakon ambaliya daga kogin Kilange da kogin Faro. Mazaunan garin...

Sojoji sun ceto mutane 6 daga cikin É—aliban jami’ar Gusau da aka sace

Sojoji sun ceto dalibai mata shida daga cikin daliban Jami'ar Gwamnatin Tarayya dake Gusau da aka bada rahoton yan bindiga sun yi garkuwa da...

Ƴan bindiga sun yi garkuwa da É—aliban Jami’ar Tarayya da ke Gusau

An sace wasu daliban jami’ar tarayya ta Gusau da ba a tantance adadinsu ba da sanyin safiyar Juma’a. ‘Yan ta’addan masu yawan gaske sun...

Yan sanda sun gano haramtacciyar masana’antar Æ™era makamai Cross River

Rundunar yan sandan jihar Rivers ta ce ta bankaɗo wata haramtacciyar masana'antar ƙera bindigogi da nakiyoyi dake garin Osomba a karamar hukumar Akamkpa ta...