Yan sanda a jihar kebbi sun kama wani mutum da ya yiwa yarinya yar shekara 12 fyade

Rundunar yan sandan jihar Kebbi ta kama wani mutum mai suna Saidu Sani wanda aka fi sani da Dankahuwa kan laifin yiwa wata yarinya fyade mai suna Amina Isiya a karamar hukumar Aliero ta jihar.

A cewar yan sandan wani danuwan yarinyar ne mai suna Yushau Adamu ya kai rahoton faruwar lamarin wurin yan sanda.

Wanda ake zargi ya hilaci ƙaramar yarinyar zuwa ɗakinsa inda ya yi lalata da ita.

Mai magana da yawun rundunar yan sandan jihar, SP Nafiu Abubakar a cikin sanarwar da ya fitar ya ce wanda ake zargi bayan ya aikata fyade ya yi barazanar kashe yarinyar idan ta fadawa wani abun da ya faru.

Ya kara da cewa tuni aka shirya gurfanar da wanda ake zargin a gaban kotu.

More News

Ƴan sanda sun kama mutane 50 kan rikicin da ya faru a wata kasuwa a Lagos

Rundunar Æ´an sandan jihar Legas ta kama mutane sama da 50 da ake zargin suna da hannu rikicin da ya faru a kasuwar Ile...

Ƴan Sanda sun kama wanda ya shirya kai harin jirgin ƙasar Abuja-Kaduna a shekarar 2022

Rundunar ƴan sandan Najeriya ta ce jami'anta sun kama wani mutum mai suna Ibrahim Abdullahi wanda ake zargi da kitsa harin jirgin ƙasar da...

Ƴansanda sun kama wanda ya kitsa harin da aka kai wa jirgin ƙasa a Kaduna

Rundunar ‘yan sandan Najeriya a ranar Alhamis, ta sanar da kame wanda ake zargin ya shirya harin da aka kai a jirgin ƙasan Abuja-Kaduna...

Sojoji Sun Ceto Mutane Daga Hannun Masu Garkuwa Da Mutane A Filato

Dakarun rundunar Operation Safe Haven dake aikin tabbatar da tsaro a jihar Filato da wani É“angare na jihar Kaduna sun samu nasarar ceto mutane...