‘Yan Kato Da Gora a Shiyar Arewa Maso Gabashin Najeriya Sun Samu Horo

Kungiyar ‘yan kato da gora ta Civilian JTF da Vigilante daga jihohin Borno, Adamawa da kuma Yobe, sune suka sami horon yadda za su taimaka wa kokarin gwamnati wajen yaki da Boko Haram da inganta zamanta kewar al’ummomin yankin.

Cibiyar koyar da shugabanci da zama ‘dan kasa na gari, dake birnin Jos, ita ce ta horar da matasan su dari biyar da saba’in da bakwai (577).

Darakta janar na cibiyar, Mr Jonah Bawa, ya ce sun horar da matasan ne kan yadda zasu yi mu’amula da mutane da sauya tunaninsu, don taimaka wa kasarsu.

Wasu da suka sami horon sun bayyana cewa zasu yi amfani da abin da suka koya don samar da zaman lafiya.

Mai hada shirye-shirye a kungiyar Civilian JTF na jahar Borno, Abba Aji, ya ce gwamnati za ta ci gaba da kula da wadan da suka sadaukar da rayukansu wajen samar da tsaro a jihar.

Wakilin hukumar raya kasashe ta Majalisar Dinkin Duniya a Najeriya, Mista Mathew Alao, ya yi fatan wadan da suka sami horon za su yi amfani da abin da suka koya wajen sasanta al’umma da inganta tattalin arzikin kasa.

More News

APC ta dakatar da Ganduje a matakin gunduma

Mambobin jam'iyyar APC a mazabar da ke Karamar Hukumar Dawakin Tofa a Jihar Kano sun dakatar da Shugaban Jam’iyyar APC na kasa Abdullahi Ganduje. ...

Yadda rikici a kan gishirin N20 ya yi sanadiyyar mutuwar wani mutum a Kano

Wani magidanci mai suna Zakari Hamza mai shekaru 45, ya gamu da ajalinsa a hannun kanen matarsa, wani Magaji Salisu saboda gishirin N20. Dan marigayin,...

Sojoji Sun Kashe Mayaƙan IPOB 5

Dakarun rundunar sojan Najeriya da kuma ta rundunar sojan ruwan Najeriya a ranar Talata sun kashe mayaƙan ƙungiyar IPOB guda biyar a yayin musayar...

Ɗan agajin Izala ya samu lambar yabo, kujerar hajji, kyautar mota bayan ya tsinci naira miliyan 100 ya mayar wa mai su

Salihu AbdulHadi Kankia, mamba ne na kungiyar agaji ta kungiyar Jama’atu Izalatil Bid’ah Wa Iqamatus Sunnah (JIBWIS), ya samu yabo da tukuicin mayar da...