‘Yan Kato Da Gora a Shiyar Arewa Maso Gabashin Najeriya Sun Samu Horo

Kungiyar ‘yan kato da gora ta Civilian JTF da Vigilante daga jihohin Borno, Adamawa da kuma Yobe, sune suka sami horon yadda za su taimaka wa kokarin gwamnati wajen yaki da Boko Haram da inganta zamanta kewar al’ummomin yankin.

Cibiyar koyar da shugabanci da zama ‘dan kasa na gari, dake birnin Jos, ita ce ta horar da matasan su dari biyar da saba’in da bakwai (577).

Darakta janar na cibiyar, Mr Jonah Bawa, ya ce sun horar da matasan ne kan yadda zasu yi mu’amula da mutane da sauya tunaninsu, don taimaka wa kasarsu.

Wasu da suka sami horon sun bayyana cewa zasu yi amfani da abin da suka koya don samar da zaman lafiya.

Mai hada shirye-shirye a kungiyar Civilian JTF na jahar Borno, Abba Aji, ya ce gwamnati za ta ci gaba da kula da wadan da suka sadaukar da rayukansu wajen samar da tsaro a jihar.

Wakilin hukumar raya kasashe ta Majalisar Dinkin Duniya a Najeriya, Mista Mathew Alao, ya yi fatan wadan da suka sami horon za su yi amfani da abin da suka koya wajen sasanta al’umma da inganta tattalin arzikin kasa.

More News

Tayoyin jirgin saman Max Air sun fashe a Yola

Jirgin saman kamfanin Max Air ƙirar Boeing 737 mai rijistar namba 5N-ADB dake ɗauke da fasinjoji 118 da ma'aikata 6 ya gamu da matsala...

Ɗan majalisar wakilai ta tarayya ya mutu

Hon. Olaide Akinremi Jagaba mamba a majalisar wakilai ta Najeriya dake wakiltar mazaɓar Ibadan North a majalisar ya mutu. Kawo yanzu babu cikakken bayani kan...

Gwamnan Kano ya sanya hannu kan dokar yin gwajin lafiya kafin aure

Gwamnan jihar Kano, Engr Abba Kabir Yusuf ya sanya hannu kan wata doka za ta tilastawa masu yin aure yin wasu gwaje-gwajen lafiya gabanin...

An kashe kwamandan soji a Katsina

An kashe kwamandan sojoji na wani sansanin soji da ke Sabon Garin Dan’Ali a karamar hukumar Danmusa a jihar Katsina a wani harin kwantan...