Yan bindiga sun yi garkuwa da mutane 70

Yan bindiga sun harbe mutane hudu tare da yin garkuwa da wasu 70 a wasu kauyuka dake karamar hukumar Sabon Birni ta jihar Sokoto a tsakanin ranar Lahadi zuwa Litinin.

Wata majiya dake yankin ta fadawa jaridar Daily Trust cewa mutane hudun da aka kashe manoma ne da aka kashe a gonakinsu.

Wani tsohon shugaban karamar hukumar, Idris Danchadi ya bayyana cewa yan bindigar sun kuma sace manoma 70.

Ya ce mutane 19 aka sace daga kauyen Tsamaye sai kauyukan Mazau da Marina inda aka sace 11 a kowanne.

Ya kara da cewa yara 7 yayan wani da ake kira Alhaji Malam aka sace daga kauyen Katume 8 kuma daga kauyen Garki da Yar’adua.

Danchadi ya kara da cewa mutane 15 aka sace daga kauyen unguwar Lalle 7 kuma daga Dangawo.

More News

Zanga-zanga: An jibge Æ´an sanda 4200 a Abuja

Rundunar Æ´an sandan birnin tarayya Abuja ta tura Æ´an sanda 4200 gabanin zanga-zangar da za a gudanar a cikin watan Agusta. Kamar yadda masu shirya...

Kamfanin NNPC ya shirya daukar karin ma’aikata

Kamfanin mai na Nigerian National Petroleum Company Limited ya shirya daukar karin ma’aikata.Kakakin kamfanin na NNPC, Olufemi Soneye, ya tabbatar da hakan a wata...

Ya kamata matasa su yi haÆ™uri zanga-zanga ba ita ce mafita ba – Sarkin Zazzau

Sarkin Zazzau, Mai Martaba Ahmed Nuhu Bamalli ya ce matasa su ƙara haƙuri da gwamnatin tarayya su janye zanga-zangar da suka shirya gudanarwa a...

Zanga-zanga: Tinubu ya gana da gwamnonin APC

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya gana da gwamnonin da aka zaɓa ƙarƙashin jam'iyar APC. Taron ganawar da aka gudanar a fadar shugaban ƙasa ta...