Yan bindiga sun yi garkuwa da mutane 70

Yan bindiga sun harbe mutane hudu tare da yin garkuwa da wasu 70 a wasu kauyuka dake karamar hukumar Sabon Birni ta jihar Sokoto a tsakanin ranar Lahadi zuwa Litinin.

Wata majiya dake yankin ta fadawa jaridar Daily Trust cewa mutane hudun da aka kashe manoma ne da aka kashe a gonakinsu.

Wani tsohon shugaban karamar hukumar, Idris Danchadi ya bayyana cewa yan bindigar sun kuma sace manoma 70.

Ya ce mutane 19 aka sace daga kauyen Tsamaye sai kauyukan Mazau da Marina inda aka sace 11 a kowanne.

Ya kara da cewa yara 7 yayan wani da ake kira Alhaji Malam aka sace daga kauyen Katume 8 kuma daga kauyen Garki da Yar’adua.

Danchadi ya kara da cewa mutane 15 aka sace daga kauyen unguwar Lalle 7 kuma daga Dangawo.

More News

EFCC na neman Yahaya Bello ruwa a jallo

Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati (Economic and Financial Crimes Commission) ta bayyana tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello a matsayin...

Mutane da dama sun mutu bayan motar fasinja ta taka bam a Borno

Akalla mutane 16 ne ake fargabar sun mutu yayin da wasu 20 suka jikkata bayan wata motar fasinja da ke kan titin Baga-Kukawa a...

Sojoji Sun Ceto Lydia Simon ĆŠaya Daga Cikin Ćłan Matan Chibok

Dakarun sojan Najeriya dake aiki da rundunar samar da tsaro ta Operation Desert Sanity III sun samu nasarar ceto, Lydia Simon É—aya daga cikin...

Gwamna da ƴansanda sun daƙile yunkurin EFCC na kama Yahaya Bello

A ranar Laraba ne Gwamnan Jihar Kogi, Usman Ododo, ya dakile wani yunkurin da Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati ta...