Yan bindiga sun yi garkuwa da mutane 70

Yan bindiga sun harbe mutane hudu tare da yin garkuwa da wasu 70 a wasu kauyuka dake karamar hukumar Sabon Birni ta jihar Sokoto a tsakanin ranar Lahadi zuwa Litinin.

Wata majiya dake yankin ta fadawa jaridar Daily Trust cewa mutane hudun da aka kashe manoma ne da aka kashe a gonakinsu.

Wani tsohon shugaban karamar hukumar, Idris Danchadi ya bayyana cewa yan bindigar sun kuma sace manoma 70.

Ya ce mutane 19 aka sace daga kauyen Tsamaye sai kauyukan Mazau da Marina inda aka sace 11 a kowanne.

Ya kara da cewa yara 7 yayan wani da ake kira Alhaji Malam aka sace daga kauyen Katume 8 kuma daga kauyen Garki da Yar’adua.

Danchadi ya kara da cewa mutane 15 aka sace daga kauyen unguwar Lalle 7 kuma daga Dangawo.

More News

Qatar za ta taimaki marayu a Najeriya

Gwamnatin kasar Qatar ta bayyana cewa za ta ba da tallafi ga yara marayu sama da 1,000 da suka rasa iyayensu saboda rikicin Boko...

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miĆ™ata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...

An dakatar da ayyukan kamfanin jiragen sama na Dana Air

Festus Keyamo, ministan harkokin sufurin jiragen sama ya umarci hukumar FAAN dake lura da sufurin jiragen sama a Najeriya ta dakatar da ayyukan kamfanin...

Yahaya Bello Ya Bayyana Dalilan Da Ya Hana Shi Bayyana A Gaban Kotu

Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya ce tsoron kamun  hukumar EFCC dake yaĆ™i da yiwa tattalin arzikin Ć™asa ne ya hana shi bayyana...