Yan bindiga sun sace kwamishinan yaÉ—a labarai na Benue

Yan bindiga sun yi garkuwa da, Matthew Abo Kwamishinan Yada Labarai, Al’adu da Yawon Bude Ido na jihar Benue.

An yi garkuwa da Abo a gidansa dake garinsu na Zaki-Biam a karamar hukumar Ukum ta jihar ranar Lahadi da daddare.

Kwamishinan ya karbi rantsuwar kama aiki ne a matsayin mamba a majalisar zartarwar jihar a ranar 29 ga watan Agusta.

Ya fito ne daga karamar hukumar Ukum da tayi kaurin suna wajen tashin hankali.

Shedun gani da ido sun ce wasu yan bindiga ne akan babura suka sace kwamishinan daga gidansa dake Zaki-Biam kauyen da yayi fice kan kasuwan doya mafi girma a Najeriya.

More News

An sake gano gawar wani shugaban Fulani da ya ɓata a jihar Filato

An gano gawar wani Arɗon Fulani, Umar Ibrahim da ya ɓace a cikin wata rijiya dake kauyen Jokom a ƙaramar hukumar Mangu ta...

An kama Æ´an kungiyar IPOB 18 da ake zargi da kisan Æ´an sanda

Rundunar yan sandan jihar Imo ta kama mutane 18 da ake zargi da zama yan kungiyar IPOB da suke da hannu a kisan Æ´an...

Kotun ɗaukaka ƙara ta tabbatar da zaɓen gwamnan jihar Sokoto

Kotun ɗaukaka ƙara dake Abuja ta tabbatar da zaɓen, Ahmed Aliyu a matsayin gwamnan jihar Sokoto. Rukunin alkalan kotun su uku sun yi watsi da...

Kotun ɗaukaka ta soke zaɓen shugaban majalisar dokokin jihar Kaduna

Kotun ɗaukaka ƙara dake Abuja, ta soke zaɓen kakakin majalisar dokokin jihar Kaduna, Yusuf Liman. Alkalan kotun uku sun bayar da umarni da a sake...