Yan bindiga sun sace kwamishina a jihar Nassarawa

Wasu yan bindiga da ba a san ko suwaye ba sun sace Mallam Yakubu Lawal Kwamishinan Yada Labarai Al’adu da Yawon Bude Ido na jihar Nasarawa.

Rahotanni sun nuna cewa an sace Lawan ne daga gidansa dake Nasarawa Eggon ranar Litinin da daddare bayan musayar wuta da yan bindigar.

Wani dan uwan kwamishinan da ya nemi a saka ya sunansa ya tabbatar da faruwar lamarin inda ya ce yan bindigar da suka sace kwamishinan sun zo ne dauke da manyan bindigogi.

Kawo yanzu dai rundunar yan sandan jihar Nasarawa ba ta fitar da wata sanarwa ba kan faruwar lamarin.

More News

An sake gano gawar wani shugaban Fulani da ya ɓata a jihar Filato

An gano gawar wani Arɗon Fulani, Umar Ibrahim da ya ɓace a cikin wata rijiya dake kauyen Jokom a ƙaramar hukumar Mangu ta...

An kama Æ´an kungiyar IPOB 18 da ake zargi da kisan Æ´an sanda

Rundunar yan sandan jihar Imo ta kama mutane 18 da ake zargi da zama yan kungiyar IPOB da suke da hannu a kisan Æ´an...

Kotun ɗaukaka ƙara ta tabbatar da zaɓen gwamnan jihar Sokoto

Kotun ɗaukaka ƙara dake Abuja ta tabbatar da zaɓen, Ahmed Aliyu a matsayin gwamnan jihar Sokoto. Rukunin alkalan kotun su uku sun yi watsi da...

Kotun ɗaukaka ta soke zaɓen shugaban majalisar dokokin jihar Kaduna

Kotun ɗaukaka ƙara dake Abuja, ta soke zaɓen kakakin majalisar dokokin jihar Kaduna, Yusuf Liman. Alkalan kotun uku sun bayar da umarni da a sake...