
Yan bindiga sun kashe, Mallam Lawali Musa wani ma’aikacin lafiya a wani hari da suka kai da daddare a garin Moriki dake karamar hukumar Zurmi ta jihar Zamfara ranar Talata.
Yan bindiga sun kuma samu nasarar yin garkuwa da mutane 8 daga garin a harin da suka kai wanda ya ɗauki tsawon minti kamar yadda wasu mazauna garin suka faɗawa jaridar 21 Century Chronicles.
A cewar majiyar an kashe Lawal ne bayan da yaki yarda yan bindigar su yi garkuwa da shi lokacin da suka shiga gidansa.
“Sun so daukarshi zuwa cikin daji amma ya ce ba zai bi su ba abun da ya jawo yan bindigar su ka har be shi,” a cewar wani abokin aikinsa a hirar da ya yi jaridar 21 Century Chronicles.
Huɗu daga cikin mutane uku da aka yi garkuwa da su ƴaƴan marigayin ne.
Kawo yanzu rundunar yan sandan jihar Zamfara bata fitar da wata sanarwa ba kan harin.

