Yan bindiga sun kashe wani lauya a Zamfara

Wasu da ake zargin yan bindiga ne sun kashe, Ahmad Kwatarkwashi wani jami’in Kungiyar Lauyoyin Najeriya ta NBA a gidansa dake karamar hukumar Bungudu ta jihar Zamfara.

Da yake tabbatar da faruwar lamarin, Junaidu Abubakar shugaban kungiyar ta NBA shiyar Gusau ya ce yan bindigar sun kai wa marigayin farmaki ne cikin dare da misalin karfe 3 a ranar Laraba

Kafin mutuwar sa marigayin ya kasance jamiin walwala na kungiyar ta NBA reshen Gusau.

Abubakar ya ce yan bindigar sun lakadawa matar marigayin duka a kokarin a tilasata mata ta nuna inda yake hakan yasa marigayin ya fito daga inda ya buya.

Bayan da yaji ihun matar ne ya sa ya bayyana kansa inda suka ja shi waje suka sassare shi da hakan kuma ya yi sanadiyar mutuwarsa.

More News

Tinibu ya aikawa da majalisar dattawa sunaye 7 na  ministocin da zai naÉ—a

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya yi kira ga majalisar dattawa da ta tabbatar da sunayen mutane 7 da ya tura majalisar da zai...

Gwamnatin Abia za ta fara biyan albashi mafi maranci na naira 70,000 a watan Oktoba

Gwamnatin Jihar Abia ta sanar da cewa za ta fara biyan sabon albashi mafi karanci na naira 70,000 ga ma’aikatanta daga watan Oktoba 2024.Kwamishinan...

Sojoji sun lalata haramtattun matatun mai 32 a yankin Neja Delta

Dakarun sojan Najeriya na runduna ta 6 dake Fatakwal sun samu nasarar lalata haramtattun matatun man fetur 32 tare da ƙwace lita 250,000 na...

An gudanar da bikin cikar Kwankwaso shekara 68.

Tarin magoya baya da kuma abokanan siyasar tsohon gwamnan jihar Kano, Sanata Rabi'u Kwankwaso ne suka halarci taron lakca da aka shirya domin bikin...