Yan bindiga sun kashe mutum 4 tare da sace wasu mutane 18 a Sokoto

A ƙalla mutane huɗu aka kashe bayan da wasu da ake zargin yan bindiga ne suka kai hari kan kauyen Giyawa dake karamar hukumar Goronyo ta jihar Sokoto.

A cewar Ahmad Rufa’i mai magana da yawun rundunar yan sandan jihar maharan sun kuma yi awon gaba da wasu mutane 18.

Rufa’i ya kara da cewa 7 daga cikin mutanen da aka sace sun kubuta inda suka dawo kauyen.

Ya kuma kara da cewa jami’in tsaro na bin sawun yan bindigar.

Jihar ta Sokoto na daga cikin jihohin da suke yankin arewa maso yamma dake fama da hare-haren yan bindiga.

More News

Sojoji sun lalata haramtattun matatun mai 32 a yankin Neja Delta

Dakarun sojan Najeriya na runduna ta 6 dake Fatakwal sun samu nasarar lalata haramtattun matatun man fetur 32 tare da ƙwace lita 250,000 na...

An gudanar da bikin cikar Kwankwaso shekara 68.

Tarin magoya baya da kuma abokanan siyasar tsohon gwamnan jihar Kano, Sanata Rabi'u Kwankwaso ne suka halarci taron lakca da aka shirya domin bikin...

Faruk Lawan ya kammala zaman gidan yarin Kuje

An sako tsohon É—an majalisar wakilai ta tarayya, Hon Faruk Lawan daga gidan yarin Kuje bayan da ya kammala zaman gidan yarin na shekaru...

Sojojin Najeriya Sun Musanta Jita-jitar Mutuwar Babban Hafsan Sojojin Ƙasa, Laftanar Janar Taoreed Lagbaja

Daga Sabiu AbdullahiRundunar Sojojin Najeriya ta karyata rahotannin da ke yawo a kafafen sada zumunta cewa Babban Hafsan Sojojin Ƙasa, Laftanar Janar Taoreed Lagbaja,...