Akalla mutane 7 aka kashe a ranar Juma’a lokacin da wasu yan bindiga suka kai hari kan wasu masallata a kauyen Saya-Saya dake karamar hukumar Ikara ta jihar Kaduna.
Mansir Hassan mataimakin mai magana da yawun rundunar yan sandan jihar ya ce an kai harin ne da misalin karfe 08:00 na dare lokacin da mutanen suke sallar isha’i.
Hassan ya ce yan bindigar sun harbe mutane 6 a kauyen Saya-Saya inda suka karasa kauyen Tashar Dauda suka kashe karin wani mutum guda a masallaci.
Ya ce mutane uku sun samu rauni a lokacin farmaki kuma yan bindigar sun yi awon gaba da babura huÉ—u.
Mataimakin mai magana da yawun rundunar yan sandan ya ce maharan sun samu nasarar tserewa kafin jami’an tsaro su karasa wurin da lamarin ya faru.