‘Yan bindiga sun kai hari jirgin Abuja zuwa Kaduna’

Fasinjojin da ke ke cikin jirgin kasan da ‘yan bindiga suka kai wa hari a kan hanyarsu ta zuwa Kaduna daga Abuja sun bayyana yanayi irin na dimauta da suka tsinci kansu a ciki.

Bayanai sun nuna cewa kimanin mutum 1000 ne a cikin jirgin, wanda aka kai wa hari ranar Litinin da daddare.

Rahotanni sun ce an sace mutane da dama sannan an kashe wasu, abin da ya jijjiga iyalai da ‘yan uwan fasinjojin da ke cikin jirgin.

Daya daga cikin fasinjojin da ya sha da kyar ya shaida wa BBC yanayi na ukuba da suka tsinci kansu da yanayi na rudani da tashin hankali a lokaci guda.

Babu dai wasu cikakkun bayanai kawo yanzu kan yawan fasinjoji da suka rasa rayukansu ko adadin wadanda suka jikkata.

Sai dai wasu bayanan daga fasinjoji na cewa an ga gawawwaki da dama sannan mutane da dama sun jikkata daga harbe-harben bindiga.

Usaman Mu’azu Saleh da ke kan jirgin ya shaida wa BBC cewa suna cikin tafiya kawai suka ji karar abu kamar bam ya tashi ya kuma girgiza jirgin, hakan na faruwa ba jimawa aka soma harbe-harbe.

Ya ce ya ga gawawwaki da dama, kuma abin ya fi shafar mata, saboda shi kansa a kan idonunsa ya ga gawawwakin mata uku zuwa hudu da aka harba.

“An kwashe fasinjoji da dama sun soma harin ne daga taragon baya, sai suka rinka bi tarago-tarago suna kwashe mutane da kashe na kashewa.

“Tun da misalin karfe 8 na saura na dare abin ya faru ake ta musayar wuta har zuwa wajen 9 da rabi”.

Fasinja ya ce an shafe sama da awa guda ‘yan bindigar na cin karensu babu babbaka kafin jami’an tsaro su zo kawo musu dauki.

Hakazalika shi ma wani Fasinja Sani Ibrahim da ya kubuta da kyar ya ce ‘yan bindigar na bin kowane tarago suna haska mutane domin tantace na dauka.

Ya ce kusan babu taragon da basu shiga ba, da harbin mutanen da suka yi kokarin lalubo wayarsu da wani nau’i na abin haska wuri.

“‘Yan bindigar suna da yawa ba zan iya tantace yawansu ba, amma har matar da ke zaune kusa da ni sun kashe ta.

“Sun umarci kowa ya kwanta a kasa, kar a motsa haka wasu daga cikinmu suka rinka dabbara jan jiki a jirgin domin shiga tarago na gaba.

“Sun yi wa jirgin kawayan saboda sun zo da motarsu da suka rinka kwashe mutanen domin garkuwa da su, sun soma ne da taragon farko wanda su ne manyan kujeru.”

Malam Sani ya ce da safiyar yau Talata ya samu komawa gida, amma ya shaidi yadda fasinjoji da dama suka shiga yanayi na galabaita ga jini ta ko ina.

Ya kuma ce yana iya tuna ganin gawawwaki kusan goma da suka hada da mata da maza.

Sannan akwai bayanan da ke tabbatar da cewa harin ya shafi har wasu daga cikin fitattun mutane a kasar ciki harda tsohon gwamnan Zamfara Ibrahim Wakala wanda aka harba a cikin jirgin amma yana jinya a asibiti.

More from this stream

Recomended