Wasu ‘yan bindiga sun bude wa tawagar yakin neman zaben jam’iyyar APC wuta a garin Uyo na jihar Akwa-Ibom.
Wani dan acaba da ya shaida faruwar lamarin, ya ce ya ga mazaje uku sun fito daga mota kirar Toyota Hilux da ke ajiye a ketaren titi, kusa da inda ake gudanar da gangamin yakin neman zaben.
Ya ce mutanen sun ketara titin, su ka tsaya a mashigin harabar da ake gudanar da taron sannan su ka bude wuta kafin daga bisani su ka arce.
Mataimakin shugaban kasa Yemi Osinbajo da ya wakilci shugaba Muhammadu Buhari ya halarci wurin da lamarin ya auku, tare da shugaban jam’iyyar APC na kasa Adams Oshiomhole, da sauran jiga jigan jam’iyyar APC domin gangamin siyasa.
Jam’iyyar APC dai ta zargi jamiyyar adawa ta PDP da kasancewa da hannu a cikin harbe-harben.