Yan bindiga sun harbe wani manomi tare da sace mutane 7 a Kaduna

Ƴan bindiga sun harbe wani manomi tare da sace karin wasu mutane 7 ;maza biyu mata biyar a kauyen Unguwar Gajere dake mazabar Kutemeshi a karamar hukumar Birnin Gwari ta jihar Kaduna.

An kai wa mutanen farmaki ne lokacin da suke aiki a gonakinsu a ranar 2 ga watan Agusta.

Mamba mai wakiltar mazabar, Kakangi a majalisar dokokin jihar, Yahaya Musa shi tabbatar da faruwar lamarin inda ya ce yan bindigar sun kuma sace dabbobi a kauyukan dake kusa da garin.

A cewar sa halin da ake ciki abun damuwa ne sosai inda ya jajantawa iyalan da suka yi asarar rayukan yan uwansu.

Ya ce yawanci yan bindigar suna satar shanu a kauyukan Gwandu da Damari.

Wan mazaunin kauyen ya ce kauyukan suna yawan fuskantar hare hare daga yan bindigar inda ya ce kisan na neman zama abin dake faruwa kullum. Ya yi kira da akawo musu dauki daga hukumomin da abin ya shafa.

More News

Gwamnatin Abia za ta fara biyan albashi mafi maranci na naira 70,000 a watan Oktoba

Gwamnatin Jihar Abia ta sanar da cewa za ta fara biyan sabon albashi mafi karanci na naira 70,000 ga ma’aikatanta daga watan Oktoba 2024.Kwamishinan...

Sojoji sun lalata haramtattun matatun mai 32 a yankin Neja Delta

Dakarun sojan Najeriya na runduna ta 6 dake Fatakwal sun samu nasarar lalata haramtattun matatun man fetur 32 tare da ƙwace lita 250,000 na...

An gudanar da bikin cikar Kwankwaso shekara 68.

Tarin magoya baya da kuma abokanan siyasar tsohon gwamnan jihar Kano, Sanata Rabi'u Kwankwaso ne suka halarci taron lakca da aka shirya domin bikin...

Faruk Lawan ya kammala zaman gidan yarin Kuje

An sako tsohon É—an majalisar wakilai ta tarayya, Hon Faruk Lawan daga gidan yarin Kuje bayan da ya kammala zaman gidan yarin na shekaru...